Najeriya
Mutane 37 sun mutu sanadiyar cutar "Bakon dauro" a Najeriya
Gwamnatin Najeriya ta zargi iyayen yara kan matsalar da aka samu na barkewar cutar Bakon dauro, da ta lakume rayukan yara 37 a Arewacin kasar. Ministan kasa a ma’aikatar lafiya, Dakta Muhammaed Ali Pate, ya shaidawa Jaridar Daily Trust cewar, rashin yin rigakafi shi ke haifar da kamuwa da cutar da kuma mace mace.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
Ya zuwa yanzu daruruwan yara suka kamu da cutar a Arewacin kasar, wanda ke nuna yara 1,260 suka kamu da cutar a Katsina, a jahar Kano mutane 800 sai jahar Yobe inda mutane 361 suka kamu da cutar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu