Masar
Har yanzu al-Sisi ne Ministan tsaron kasar Masar
Yayin da a yau Asabar aka rantsar da sabuwar majalisar zartawan kasar Masar, Shugaban Rundunar tsaron kasar Marshal Abdel Fattah al-Sisi, ya ci gaba da rike mukamin ministan tsaron kasar. Dama ana ta rade radin al-Sisi zai tsaya takarar shugabancin kasar, a zaben da za a yi a wani lokaci cikin wannan shekarar.An fidda Jerin sunayen sabbin Ministocin da priminista Ibrahim Mahlab ke jagoranta ne, bayan da gwamnatin da ta shude ta yi murabus a ranar Litinin da ta gabata, sakamakon sukan da take sha, saboda matalolin tattalin arziki da tashe tashen hankula.
Wallafawa ranar: