Gwamnatin Gombe ta musanta harin Bom
Akalla mutane uku aka ruwaito sun mutu sakamakon fashewar wani abu makamancin Bom da aka samu a garin Gombe kusa da babbar kofar da ke zuwa gida, kuma masaukin Gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Ibrahim Hassan Dankwambo.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Akwai dai rahotanni masu karo da juna game da musabbabin faruwar fashewar da wasu suka danganta da Bom wanda ya tashi a wata Motar sulke ta masu gadi.
A cikin rahoton Shehu Saulawa, Shedun gani da ido sun ce fashewar ta turnike sararin samaniya da hayaki. Amma kakakin gwamnanatin Jahar Gombe Malam Junaidu Usman Abubakar ya musanta bom ne ya tashi a harabar gidan Gwamnan Jahar.
Rahoton Shehu Saulawa daga Bauchi
Wasu majiyoyi a Najeriya sun ce akalla mutane uku suka mutu a sakamakon fashewar. Amma Zuwa yanzu babu wani bayani daga rundunar ‘Yan sandan Jahar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu