Isa ga babban shafi
Guinea Bissau

Shugaban Guinea Bissau ya rusa gwamnatinsa

Shugaban kasar Guinea Bissau Jose Mario Vaz ya rusa gwamnatinsa a yau Alhamis saboda sabani tsakanin shi da Firiminista Domingos Simoes Pereira. Kafofin yada labaran Gwamnati ne suka bayar da sanarwar rusa gwamnatin.

Shugaban Guinée-Bissau, José Mario Vaz
Shugaban Guinée-Bissau, José Mario Vaz AFP PHOTO / SIA KAMBOU
Talla

Sabani tsakanin shugaban kasar da Firaministansa na neman jefa kasar cikin rudanin siyasa inda tun dawo da mulkin dimokuradiya bayan juyin mulkin da Sojoji suka yi a 2012 shugabannin ke rikici da juna.

A watan Yulin 2014 ne aka kafa gwamnatin Pereira bayan Jose Mario Vaz ya lashe zaben shugaban kasa karo na biyu a watan Mayu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.