Isa ga babban shafi
Sudan-UN

An saki wasu jami'an tsaro a Darfur

Yan tawayen yankin Darfur na kasar Sudan sun saki wasu jami’an tsaron kasar 18 da suka share tsawon lokaci tsare a hannun su, bayan da kungiyar bayar da agaji ta kasa da kasa Red Cross ta shiga tsakani. Ofishin kungiyar ta Red Cross a yankin na Darfur ya ce an saki sojoji 13, ‘yan sanda uku da kuma fararen hula biyu inda tuni suka isa garin Nyala fadar gwamnatin lardin Kudancin Darfur. 

Kasar Sudan da yankin Darfur
Kasar Sudan da yankin Darfur Reuters/路透社
Talla

A daidai lokacin  wanan juma’a ne kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya zai gudanar da zama na musamman a game da halin da ciki a Sudan ta Kudu, sakamakon fadan da ake ci gaba da yi tsakanin dakarun gwmanati da na ‘yan tawaye duk da cewa bangarorin biyu sun kulla yarjejeniyar zaman lafiya a tsakaninsu.

Kasar Amurka ce dai ta gabatar da bukatar gudanar da zaman a gaban kwamitin mai kasashen 15, kuma akwai yiyuwar sanya takunkuman kan wadanda ke da hannu a rikicin.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.