Isa ga babban shafi
Sudan-UN

Dubban mutane sun fice yankin Darfur na Sudan

Majalisar Dinkin Duniya sama da mutane dubu dari da Talatin da hudu suka fice yankin Darfur na kasar Sudan saboda gwabza fada ake yi tsakanin dakarun Gwamnati da ‘Yan tawaye.

A rana Daruruwa ke ficewa yankin Darfur
A rana Daruruwa ke ficewa yankin Darfur REUTERS/Albert Gonzalez Farran/ys
Talla

Jami’ar hukumar jinkai ta Majalisar Dinkin Duniya tace mutanen sun fice saboda fada da ake yi tsakanin Sojojin Gwamnati da ‘Yan tawaye a yankin Jebel Marra mai tsaunika.

Yankin Jebel Marra dai ya dade karkashin ikon ‘Yan tawayen SLA da suka jima suna fada da gwamnati tun a 2003.

Majalisar Dinkin Duniya tace fararen hula kimanin 19,000 suka fice Jihar arewacin Darfur yayin da 15,000 suka tsere daga Jihar tsakiyar Darfur.

Kuma yawancin wadanda suka tsere wa rikicin Mata ne da yara kanana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.