Isa ga babban shafi
Ebola

An sake kawar da Ebola a Guinea

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO tace an kawo karshen barkewar cutar Ebolar da aka sake samu a kasar Guinea, amma hukumar ta yi gargadi akan cutar na iya sake bulla.

Ebola ta yi kisan mutane a kasashen Liberia da Guinea da Saliyo
Ebola ta yi kisan mutane a kasashen Liberia da Guinea da Saliyo KENZO TRIBOUILLARD / AFP
Talla

Wakilin hukumar Aboubacar Gaye ya ce an sallami mutumin da ya kamu da cutar na karshe a watan Afrilu kuma yanzu haka an kwashe kwanaki 42 ba tare da samun wani ya kamu da cutar ba.

Sakoba Keita, jami’in yaki da cutar a Guinea ya ce mutane 3,814 aka tabbatar sun kamu da cutar yayin da kimanin 2,544 suka mutu.

Cutar dai ta sake bulla a kasashen Guinea da Liberia da Saliyo bayan ta yi kisan dubban mutane a kasashen.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.