Isa ga babban shafi
Eritrea-Habasha

Ban Ki-moon ya shawarci Habasha da Eritrea su kai zuciya nesa

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki Moon ya bukaci kasashen Habasha da Eritrea da su kai zuciya nesa domin kawo karshen hare haren da ake samu akan iyakokinsu.

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon ©REUTERS/Heinz-Peter Bader
Talla

Mai Magana da yawun Sakataren, Stephaine Dujjaric yace Ban ya bayyana haka ne lokacin da ya gana da Firaminsitan Habasha Hailemariam Desalegn a Brussels, yayin da mataimakin Sakatare Janar Jan Eliasson kuma ya tattauna da ministan harkokin wajen Eritrea ta waya.

Ban ya bukaci kasashen biyu su warware sabanin su ta hanyar tattaunawa maimakon daukar makamai.

Kasashen dai na rikici ne kan garin Badme da ya yi iyaka da kasashen biyu wanda Majalisar Dinkin Duniya ta ba Eritrea amma har yanzu yana karkashin ikon Habasha.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.