Isa ga babban shafi
Honduras

Honduras Ta Kama Bakin Haure 109 Daga Kasashen Afrika

Gwamnatin kasar Honduras sun karas da cewa su na tsare da wasu bakin haure 109 daga kasashen Africa da ke kokarin tsallakawa zuwa yankin Tsakiyar Amurka don tafiya cikin kasar Amurka.

Shugaba Juan Orlando Hernández na kasar Honduras
Shugaba Juan Orlando Hernández na kasar Honduras Reuters
Talla

Wani Jami’in Hukumar kula da shige da fice na kasar ya bayyanawa Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP cewa suna duba yiwuwar barin mutanen  su tafi ko kuma a tsare su.

Mai Magana da yawun Hukumar kula da shige da ficen ya bayyana cewa mutanen sun hada da manya 100, da kananan yara tara da suka fito daga kasashen Janhuriyar Democradiyya ta Congo, Mali, Senegal da Burkina Faso kuma an kama su ne suna tattaki da kafa akan iyakan Honduras da kuma Nicaragua.

Jami’in mai suna Rene Vindel ya fadi cewa za’a gudanar da bincike domin tantancewa ko masu aikata laifuka ne, sannan a barsu amma kuma ba za’a bari su wuce kwanaki uku ba.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.