Honduras Ta Kama Bakin Haure 109 Daga Kasashen Afrika
Gwamnatin kasar Honduras sun karas da cewa su na tsare da wasu bakin haure 109 daga kasashen Africa da ke kokarin tsallakawa zuwa yankin Tsakiyar Amurka don tafiya cikin kasar Amurka.
Wallafawa ranar:
Wani Jami’in Hukumar kula da shige da fice na kasar ya bayyanawa Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP cewa suna duba yiwuwar barin mutanen su tafi ko kuma a tsare su.
Mai Magana da yawun Hukumar kula da shige da ficen ya bayyana cewa mutanen sun hada da manya 100, da kananan yara tara da suka fito daga kasashen Janhuriyar Democradiyya ta Congo, Mali, Senegal da Burkina Faso kuma an kama su ne suna tattaki da kafa akan iyakan Honduras da kuma Nicaragua.
Jami’in mai suna Rene Vindel ya fadi cewa za’a gudanar da bincike domin tantancewa ko masu aikata laifuka ne, sannan a barsu amma kuma ba za’a bari su wuce kwanaki uku ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu