Najeriya
‘Yan bindiga sun kashe mutane 15 a Zamfara
Wasu ‘Yan bindiga sun kai hari a wani kauyen Jihar Zamfara kuma sun kashe akalla mutane 15 a karamar hukumar Bungudu. Rahotanni sun ce barayin shanu ne suka kai harin tare da bude wuta kan mai uwa da abi.
Wallafawa ranar:
Talla
Kakakin rundunar ‘Yan sandan Jihar SP Sanusi Amiru ya tabbatar da mutuwar mutane 15 a harin da aka kai a kauyen Ruwan Mesa.
Zamfara dai na fama da matsalar tsaro musamman matsalar ‘Yan fashin Shanu da suka addabi makiyaya a Jihar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu