Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

Uganda tana kwashe ‘Yan kasarta daga Sudan ta kudu

Manyan motoci da tankokin yakin Sojin Uganda sun kutsa kai Sudan ta kudu domin fara kwashe fararran hula da suka makale a birnin Juba, a yayin da ake furgabar yiyuwar sake ballewar rikici a jaririyar kasar.

Rikicin Sudan ta Kudu ya raba daruruwan mutane da gidajensu
Rikicin Sudan ta Kudu ya raba daruruwan mutane da gidajensu AFP PHOTO / UNMISS/BEATRICE MATEGWA
Talla

Rikicin dai ya lafa sakamakon tsagaita wuta tsakanin dakarun gwamnatin shugaba Salva Kiir da na Mataimakin shi Riek Machar.

Bangarorin biyu sun shafe kwanaki biyar suna barin wuta a Juba babban birnin Sudan ta kudu. Amma Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin sake barkewar wani sabon rikici.

Shugaba Salva Kiir a yau Alhamis ya bukaci Sulhu da mataimakinsa Riek Machar.

Kiir ya yi wa Machar tayin tattaunawa domin tabbatar da zaman lafiya a kasar, inda ya bukaci kawo karshen zubar da jini a Sudan ta Kudu.

A safiyar alhamis din nan ne tawagar motocin sojin Uganda 50 dauke da manyan makamai suka shiga kasar domin taimakawa fararan hula da ke gudun hijira daga Juba.

Babban hafsan sojin Uganda Brigadier Leopold Kyanda ya ce tawagar na dauke da soji dubu biyu wadanda za su shafe tsawon kwananki biyu zuwa uku a Juba domin kwaso mutanen kasar saboda barazanar barkewar yaki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.