Sarkin Musulmi ya la’anci kisan da aka yi wa Lazarus Agai a Filato
Sarkin al’ummar Musulmin Najeriya Mai Alfarma Muhammad Sa’ad Abubakar na uku ya yi allawadai da kisan gillar da aka yi wa daya daga cikin manyan Sarakunan Jihar Plateau, Saf Ron Kulere Lazarus Agai.
Wallafawa ranar:
Sarkin ya bayyana haka ne lokacin da ya kai ziyara fadar shugaban Sarakunan Jihar Filato Gbong Gwom Jos, inda ya bukaci kai zuciya nesa da barin jami’an tsaro su yi aikin su wajen gano wadanda suka aikata Kisan.
Sultan Abubakar ya bayyana cewar kisan gillar na zuwa ne a dai dai lokacin da mutane a ciki da wajen Jihar Filato ke yabawa da zaman lafiyar da aka samu a Jihar.
Sai ya yi kira ga jami’an tsaro da su gaggauta zakulo wadanda suka kashe Basaraken domin ganin an hukuntasu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu