Tanzania
Girgizar kasa ta kashe mutane da dama a Tanzania
A kalla mutane 16 ne suka rasa rayukansu, in da kuma 253 suka jikkata sakamakon girgizar kasa mai karfin maki 5.7 da ta afka wa yankin arewa maso yammacin Tanzania.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugaban kasar, John Magufuli ya bayyana damuwarsa kan ibtila’in, wanda ya faru a kusa da kogin Victoria da kuma kan iyakokin Uganda da Rwanda.
Kamfanin dillancin labaran Faransa AFP ya rawaito cewa, fiye da gidaje 800 girgizar kasar ta rusa, yayin da ma’aikatan agaji ke ci gaba da neman masu sauran kwana da lamarin ya ritsa da su.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu