Tanzania
An samu asarar rayuka sakamakon girgizar kasa a Tanzania
Wata girgizar kasa mai karfin maki 5.7, da ta auku a kasar Tanzania ta yi sanadiyyar rasa rayukan mutane 13, da raunata wasu 203.
Wallafawa ranar:
Talla
Girgizar kasar ta auku ne a lardin Kagera da ke arewa maso yammacin kasar.
Kwamishinan da ke kula da yankin, Deotus Kinawilo ya ce yanzu haka an fara sallamar wasu daga cikin wadanda suka samu raunuka.
Rahotanni sun ce anji motsawar girgizar kasar a kasashen Ruwanda, Burundi, Uganda da kuma Kenya saboda karfinta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu