Merkel ta fara ziyara Mali da Nijar
Shugabar Gwamnatin Jamus Angela Merkel ta soma ziyarar kwanaki uku a Afrika inda ta fara ziyarar a Mali kafin ta je Nijar da Habasha. Shugabar za ta kuma gana da shugabannin kasashen Najeriya da Chadi a Berlin bayan ta kammala ziyarar a Afrika.
Wallafawa ranar:
Merkel zata tattauna da shugabannin kasashen uku na Afrika kan batun ‘Yan ci rani da ke kwarara zuwa Turai da kuma batun yaki da ta’addanci.
Bayan ta kammala ziyara a Habsha ne kuma zata gana da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da takwaransa na Chadi Idriss Deby a birnin Berlin na Jamus kan yaki da ta’addanci.
Tuni dai Jamus ta ce za ta bude sansanin Soji a Nijar domin taimakawa dakarun Majalisar Dinkin Duniya da ke fada da ‘Yan tawaye a Mali.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu