Zagayowar cikon shekaru biyu da korar Blaise Compaore
A Burkina Faso Gwamnatin kasar ta sanar da gudanar da addu’o’i daga ranar juma’a zuwa ranar lahadi .Wanda hakan ke karo da zagayowar cikon shekaru biyu da korar Blaise Compaore daga Shugabancin Burkina Faso.
Wallafawa ranar:
Blaise Compaore ya share shekaru 27 a shugabancin Burkina Faso ya kuma sauka bayan da yan kasar suka gudanar da zanga-zanga a harabar majalisar dokokin kasar domin hanawa yan majalisu gudanar da zaman su na kawo gyara ga kudin tsarin mulkin kasar.
A dai wajen yan siyasa sun gudanar da tarurruka da suka mayar da hankali kan gwagwarmaya da yan kasar suka yi a lokaci dama tasirin sa.
Taron da tsohon Shugaban wucin gadi Michel Kafando ya halarta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu