Isa ga babban shafi
Chad-Senegal

Hissene Habre na Chadi zai daukaka kara

Tsohon shugaban Chadi Hissene Habre na shirin daukaka kara littini mai zuwa dangane da hukuncin dauri rai-da-rai gidan yari da Kotun Hukunta masu aikata laifukan yaki ta zartas masa a Darkar na kasar Senegal.

Hissène Habré tsohon shugaban Chadi
Hissène Habré tsohon shugaban Chadi AFP PHOTO
Talla

Hissene Habre mai shekaru 73 tun a watan mayu daya gabata aka zartas masa da wannan hukuncin.

A watan juli daya gabata Kotun ta nemi ya biya diyya na kudin Amurka Dala dubu 33 ga mutanen da aka azabtar a lokacin da yake mulki.

Shi dai Hissene Habre ya ki amincewa da wannan kotun wadda Kasar Senegal da Kungiyar Tarayyar Africa suka kafa domin sauraron tuhumar da ake masa.

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.