Kamaru
Jirgi ya fadi da sojojin Kamaru
Sojojin kasar Kamaru guda 4 sun mutu bayan faduwar jirgin da suke ciki a Bogo yankin arewa mai nisa a lokacin da suke tsara kai hari kan Mayakan Boko Haram. Wata majiyar soja ta ce cikin wadanda suka rasu har da Janar Jacob Kodji da wani Kanal.
Wallafawa ranar:
Talla
Jami’in ya ce hafsoshin sojin na tafiya Yankin Bogo da ke Arewacin kasar ne lokacin da jirgin mai saukar ungulu ya fadi.
Janar Kodji ke jagoranci runduna 4 da ake yi wa lakabi da Emergence 4 da ke yaki da ‘Yan Boko Haram.
Majiyar ta ce Sojojin sun nufi dajin Waza ne domin yakar Boko Haram.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu