Isa ga babban shafi
Afrika ta Kudu

Ahmed Kathrada na Afrika ta kudu ya rasu

Daya daga cikin shugabannin yaki da mulkin wariyar launin fata a Afirka ta kudu Ahmed Kathrada kuma makusanci ga Nelson Mandela ya rasu yana da shekaru 87 a duniya.

RFI ta taba zantawa da Ahmed Kathrada a gidansa da ke  Johannesburg a ranar 21 ga watan Yunin 2013.
RFI ta taba zantawa da Ahmed Kathrada a gidansa da ke Johannesburg a ranar 21 ga watan Yunin 2013. Daniel Finnan
Talla

Kathrada na daga cikin wadanda aka daure a shekarar 1964 tare da Mandela, shari’ar da ta janyo hankalin kasashen duniya zamanin mulkin wariyar launin fata a Afrika ta kudu

Kathrada ya kwashe shekaru 26 da watanni 3 a daure, kuma ya yi shekaru 18 a gidan yarin Robben Island.

Bayan kawo karshen mulkin wariya, Kathrada ya taba zama mai ma Mandela shawara kan harakokin majalisa daga shekarar 1994 zuwa 1999.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.