Isa ga babban shafi
Rwanda

Tsutsar da ke yin ta’adi a gonakki ta bulla a Rwanda da Kenya

Hukumar samar da abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce yanzu haka tsutsar nan da ke cinye amfanin gona ta isa kasashen Rwanda da Kenya, bayan ta’adin da ta yi a wasu kasashen da ke kudancin Afirka.

Tsutar ta fara bulla a Najeriya da Togo a Bara
Tsutar ta fara bulla a Najeriya da Togo a Bara CC/Wikimedia/Sam Droege
Talla

Gwamnatin Uganda ta tabbatar da isar tsutsar gonakin kasar, inda ta zama kasa ta uku a Gabashin Afirka da ke fuskantar matsalar.

Telesphore Ndabamenye, shugaban hukumar samar da iri a Rwanda, yace tsutsar ta mamaye gonaki a Yankuna 30.

Jaridar Kenya ta ruwaito cewar tsutsar ta bulla a Yankuna 11 daga cikin Yankuna 47 da ke kasar.
Tsutar dai na yin barazana ga manoma, da suke fuskantar matsalar fari.

Tsutsar ta fi yin illa ga hatsi kamar Masara da alkama da gero da shinkafa.

Yawancin mutanen kasashen Afrika dai na dogaro ne da arzikin noma.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.