Isa ga babban shafi
Kenya

Sojojin Kenya sun kashe mayakan al-Shebab 52

Rundunar tsaron Kenya ta kashe mayakan al-Shebab 52 a wani harin konton bauna da ta kai musu a sansaninsu da ke kudsancin Somalia. 

Sojojin Kenya sun kashe mayakan al Shebab fiye da 50 a Somalia
Sojojin Kenya sun kashe mayakan al Shebab fiye da 50 a Somalia ABDI DAKAN / AU-UN IST PHOTO / AFP
Talla

Mai magana da yawun rundunar sojin kasar Kanar Joseph Owuoth ya ce, lamarin ya auku ne a yankin Badhaadhe da ke Low Juba.

Kanar Owuoth ya ce, sojojin da suka kai farmakin sun gano manyan bindigogi da kayayyakin kera bama-bamai na mayakan al-Shebab.

Kasar Kenya na da dubban dakaru a rundunar hadaka ta kungiyar kasashen Afrika da ke aikin wanzar da zaman lafiya a Somalia mai fama da barazanar tsaro saboda ayyukan ta'addancin al-Shebab.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.