Isa ga babban shafi
Somalia

Somalia na bincike kisan Minista akan kuskure

Shugaban Kasar Somalia Mohammed Abdullahi Farmajo ya bukaci gudanar da bincike kan yadda jami’an tsaro suka harbe matashin ministan ayyuka Abbas Abdullahi Siraji mai shekaru 31 bisa kuskure.

Abbas Abdullahi Sheikh Siraji Matashin Minista a Somalia da sojoji suka harbe
Abbas Abdullahi Sheikh Siraji Matashin Minista a Somalia da sojoji suka harbe Wikimedia Commons
Talla

Shugaban wanda ya katse ziyarar da ya ke yi a kasar Habasha, ya ce sun kadu da kisan saboda haka za su tabbatar an hukunta duk wanda ya ke da hannu a kisan.

Rahotanni sun ce masu tsaron fadar shugaban ne suka budewa motar ministan wuta mai suna Abbas Abdullahi Siraji da ke tuka kansa bisa tunanin ‘yan ta’adda ne.

Saboda barazanar mayakan Al Shebaab a Somalia yana da wahala Jami’in gwamnati ya fito kan titi a Mogadishu yana tuka kansa ba tare da jami’an tsaron ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.