Isa ga babban shafi
Gambia

Ana zargin Jammeh da sace Dala miliyan 50 a Gambia

Ministan shari’ar Gambia, Abubacarr Tambadou ya zargi tsohon shugaban kasar da sace kudin da ya kai Dala miliyan 50 ta hannun kamfanin sadarwar kasar, yayin da kotu ta sanya takunkumi kan kadarorinsa.

Tsohon shugaban Gambia Yahya Jammeh
Tsohon shugaban Gambia Yahya Jammeh 路透社照片
Talla

Ministan ya ce shugaba Jammeh da kansa ya bada umurnin janye kudaden daga asusun ajiyar kasar da ke Babban Bankin Gambia.

Tambadou ya ce sun yi nasarar samun umurnin kotu na rufe asusun ajiyar tsohon shugaban da kuma kadarorin da ya mallaka tare da kamfanonin da ya ke da alaka da su.

Jami’in ya ce umurnin ya shafi asusun ajiyar bankuna 88 da aka bude da sunan tsohon shugaban da kuma na kusa da shi.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.