Isa ga babban shafi
Mali

Kasashen Sahel na bukatar Kudi Euro miliyan 50 daga Tarayyar Turai don yakar masu tsananin kishin Islama

Kasashen Sahel da ke yammacin Africa sun roki  Tarayyar Turai da ta kai ma su dauki na kudaden da suka kai kudin Turai Euro miliyan 50  domin a samu a biya hakkokin Dakarun karo-karo da ke yakar masu tsananin kishin Islama da ke yankin.

Wasu Sojoji cikin shiri suna sa idanu kan muhimman wurare a Bamako na kasar Mali
Wasu Sojoji cikin shiri suna sa idanu kan muhimman wurare a Bamako na kasar Mali AFP PHOTO / ISSOUF SANOGO
Talla

Babban Hafsan Sojan Mali Janar Didier Dacko ya gabatar da wannan bukata a yau Asabar wajen taron manyan sojojin da ke yakar masu tsananin kishin Islaman.

Yankin na Sahel da suka hada da Chadi, Nijar, Burkina Faso , Mali da Mauritania sun kasance makwancin masu tsananin kishin Islama, dake hana sakat a yankin.

Babban Hafsan ya fadi a wajen taron Hafsoshin sojan kasashen biyar cewa suna bukatar kungiyar Tarayyar Turai ta kai masu tallafi.

Gobe lahadi ne kuma Ministocin tsaro na kasashen za su yi nasu taron.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.