Isa ga babban shafi
Afrika

AU ta jaddada manufar mutunta yarjejeniyar rage dumamar yanayi

Kungiyar tarayyar nahiyar Afrika AU, ta bayyana cikakken goyon bayanta ga yarjejeniyar rage dumamar yanayin da aka cimma a birnin Paris, na kasar Faransa

Hedikwatar kungiyar tarayyar nahiyar Afrika AU a birnin Addis Ababa na kasar Habasha.
Hedikwatar kungiyar tarayyar nahiyar Afrika AU a birnin Addis Ababa na kasar Habasha. REUTERS/Tiksa
Talla

Jagoran kungiyar a yanzu kuma shugaban kasar Guinea Alpha Conde, yayi ala wadai da watsin da shugaban Amurka Donald Trump yayi da yarjejeniyar a ranar Alhamis da ta gabata.

Zalika cikin jawabin da ya gabatar, Conde, ya bukaci da a sake tattaunawa kan batun rage dumamar yanayin, a taron kasashen G20 da za’a yi, a watan gobe, wanda kasar Jamus zata karbi bakunci.

A cewarsa, ko da ya ke, kasashen nahiyar Afrika basa taka muhimmiyar rawa wajen gurbata yanayi, a bayyane ta ke, nahiyar na kan gaba, a tsakanin yankunan duniya da illar dumamar yanayin ta fi shafa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.