Ruwan sama da iska ya lalata runfunan ‘yan gudun hijira a Borno
Ruwan sama da aka tafka mai tafe iska ya lalata rumfunan ‘yan gudun hijira sama da 1,000 a sansanonin da suke rayuwa a Jihar Borno, wanda ya shafi mutane kusan 5,000.
Wallafawa ranar:
Wannan ya kara fito da girman matsalar da ‘yan gudun hijirar rikicin Boko Haram ke fuskanta na rashin matsuguni mai kyau da inganci a Jihar Borno.
Rahotanni sun ce an shafe tsawon sa’o'i uku ana maka ruwan saman da iska wanda ya lalata runfunan na ‘yan gudun hijira a Maiduguri da Kaga da Konduga.
Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana damuwa kan halin da ‘yan hudun hijira za su shiga a Najeriya musamman watanni uku zuwa hudu da za a shafe ana ruwan sama.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu