Isa ga babban shafi
Kamaru

Kamaru ta tsare sojojin da ke yaki da Boko Haram

Hukumomin Kamaru sun kama akalla sojoji 30 da ke yaki da kungiyar Boko Haram saboda boren da su ka yi kan kin biyan su wasu kudade na alawus da na hutu. 

Wasu daga cikin sojojin Kamaru da ke yaki da Boko Haram
Wasu daga cikin sojojin Kamaru da ke yaki da Boko Haram AFP PHOTO / REINNIER KAZE
Talla

Sojojin sun yi bore a ranar Lahadin da ta gabata a yankin arewacin kasar, in da suka tare hanyoyin zirga-zirgar mota.

Ma’aikatar tsaron kasar ta ce, yanzu haka an kwashe sojojin daga yankin Zique zuwa birnin Yaounde, in da ake tsare da su.

Rahotanni sun ce, harkokin yau da kullum sun koma yadda aka saba bayan boren sojojin.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.