Kamaru
Kamaru ta tsare sojojin da ke yaki da Boko Haram
Hukumomin Kamaru sun kama akalla sojoji 30 da ke yaki da kungiyar Boko Haram saboda boren da su ka yi kan kin biyan su wasu kudade na alawus da na hutu.
Wallafawa ranar:
Talla
Sojojin sun yi bore a ranar Lahadin da ta gabata a yankin arewacin kasar, in da suka tare hanyoyin zirga-zirgar mota.
Ma’aikatar tsaron kasar ta ce, yanzu haka an kwashe sojojin daga yankin Zique zuwa birnin Yaounde, in da ake tsare da su.
Rahotanni sun ce, harkokin yau da kullum sun koma yadda aka saba bayan boren sojojin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu