Isa ga babban shafi
Mali

'Yan tawayen Mali sun sake kaiwa sojojin kasar hari

A kasar Mali mutane uku da suka hada da wani soji ne suka rasa rayukan su bayan da wasu yan bindiga da ake zaton yan tawayen arewacin kasar ne suka kai masu hari a wasu shigayen bicinke dake kan iyakokin Nijar, Burkina Faso da kasar ta Mali.

Tsaro a yankin arewacin Mali daga rundunar Barkhane
Tsaro a yankin arewacin Mali daga rundunar Barkhane REUTERS/Christophe Petit Tesson/Pool
Talla

Rahotani daga wani kauye mai suna Soumouni na nuni cewa an hango wasu mutane dauke da mugan makamai a kan babura inda suka habkawa wasu manoma tareda kashe biyu daga cikin su.

Duk da kokarin hukumomin kasar na shawo kan matsallolin tsaro akwai wasu yankunan kasar da yan bidinga ke ci gaba tada zaune tsaye.
Yankin Asongo ranar alhamis da ta gabata wata motar soji ta taka nakiya, inda aka samu mutuwar soji daya wasu biyu can daban suka samu rauni.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.