Isa ga babban shafi
Kamaru

Boko Haram ta kashe mutane 6 a Kamaru

Akalla mutane takwas suka mutu a wasu hare haren kunar bakin wake da aka kai a garin Kolofata yankin arewa mai nisa a Kamaru kusa da iyaka Najeriya. Cikin wadanda suka mutu har da maharan guda biyu da fararen hula shida.

Yankin arewa mai nisa a Kamaru na fama da barazanar Boko Haram
Yankin arewa mai nisa a Kamaru na fama da barazanar Boko Haram AFP PHOTO / STEPHANE YAS
Talla

An kai harin ne da marece a daidai lokacin da jama’a ke hada-hadar kasuwanci a Kolafata da ya saba fuskantar hare-hare daga ‘yan Boko Haram.

A farko watan Yunin bana an kai harin kunar bakin wake a yankin da ya kashe mutane 9, yayin da kuma aka kai wani hari a Limani kusa da Kolafata da ya kashe fararen hula biyu.

Kamaru da ke makwabtaka da Najeriya na cikin rundunar hadin guiwa da ke yaki da Boko Haram da suka addabi Yankin Arewa mai nisa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.