Har yanzu ban tsaida lokacin ritaya daga tseren gudu ba - Bolt
Zakaran tseren gudu har sau takwas a wasannin Olympics, Ussain Bolt, ya ce mai yiwuwa ne, ya cigaba da haskawa a fagen nasa, bayan kammalla gasar tseren gudu ta duniya da za’a yi cikin watan Agusta mai zuwa a birnin London.
Wallafawa ranar:
A baya Bolt mai shekaru 30, ya ce gasar tesren gudun da za’ayi a London, ita ce zata ta karshe da zai fafata, daga nan kuma a barwa ‘yan baya.
Sai dai yace bayan da ya tattauna da mai horar da shi, Glen Mills, a yanzu yana duba shawarar tsawaita cigaba da fafatawa a fagen na tseren gudu zuwa kakar wasa ta gaba.
Bolt zai fafata ne a gasar tseren gudun mita 200 a gasar duniya da za’a yi a London.
Har yanzu dai yana rike da kambun wasannin tseren gudun mita 100 da mita 200 wadanda ya lashe su tun a shekarar 2008, a birnin Biejing na kasar China.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu