Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Mourtala Mahamouda Dan Majalisa a Nijar

Wallafawa ranar:

Kotun fasalta kundin tsarin mulkin Nijar ta yi watsi da sabon kundin zaben da majalisar dokoki ta amince da shi. Inda ta bayyana soke wasu kudurori dokar zaben da dama saboda a cewar kotun sun saba wa kundin tsarin mulkn. Daga cikin ayoyin da kotun ta yi watsi da su har da wadda ke cewa idan mutum ya aikata laifi amma ya gudu zuwa waje sannan aka yanke masa hukunci, to sam ba zai iya tsayawa takara ba, da kuma wani kuduri da ke bai wa jam’iyyun siyasa karin lokaci domin yin gyara idan kotu ta gano cewa akwai kura-kurai a cikin takardun ‘yan takarar, abinda ta ce ba zai yiyu ba. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Honarabul Mourtala Mahamouda, daya daga cikin ‘yan majalisar da suka amince da kundin.

Majalisar dokokin Nijar à Niamey.
Majalisar dokokin Nijar à Niamey. AFP/Sia Kambou
Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.