Isa ga babban shafi
Senegal

Wade zai koma Senegal don yakin neman zabe

A yayin da ake shirin soma yakin neman zabe a Senegal a gobe Lahadi, tsohon shugaban kasar Abdoulaye Wade ya sanar cewa yana kan hanyarsa zuwa Dakar a ranar Litinin domin yakin neman zabe.

Tsohon Shugaban Senegal Abdoulaye Wade
Tsohon Shugaban Senegal Abdoulaye Wade AFP PHOTO / SEYLLOU
Talla

Tsohon shugaban ya shaidawa wata kafar yada labaran talabijin ta Senegal cewa zai dawo domin shiga siyasa gadan gadan inda shi ne yanzu shugaban jam’iyyar gungun ‘yan adawa ta Wattu Senegal

Sannan ya tabbatar da goyon bayansa ga dansa Karim Wade da zai tsaya takarar shugaban kasa a zaben 2019.

A ranar 30 ga watan Yuli ne za a gudanar da zaben Yan majalisu a Senegal, kuma wasu na ganin dawowar Wade barazana ne ga shugaba Macky Sall da sauran jam’iyyun da ke kawance da gwamnatinsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.