Dalilan da suka sa soji kai hari kan sansanin 'yan gudun hijira
Ma’aikatar tsaron Najeriya ta bayyana cewa taron da mutane suka yi irin na ba zata a wani sansanin ‘yan gudun hijira da ke cikin jihar Borno, shi ne babban dalilin kai harin soji ta sama a kan kuskure har aka samu asarar rayukan mutane 112 a ranar 17 ga watan janairun da ya gabata.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Har ila yau sanarwar da Manjo janar John Enenche, mai maigana da yawun ma’aikatar tsaron kasar ya fitar ta ce sansanin da aka kafa a Kala-balge, ba ya daga cikin wuraren da aka sanar da sojoji a matsayin matattarar ‘yan gudun hijira, abin da ya sa aka kai hari kansu akan kuskure.
Da farko dai an tsara za a fitar da rahoton bincike dangane da dalilin faruwar wannan kuskure ne tun a cikin watan fabarairun da ya wuce, to amma sai bayan watanni shida aka fitar da rahoton.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu