Libya
Khalifa Haftar ya tura da dakarun kasar zuwa gabar ruwan Libya
Mashal Khalifa Haftar, hafsan sojin da ke rike da muhimman yankuna a kasar Libya, ya umurci dakarunsa da su hana wa jiragen ruwan kasashen ketare matsowa kusa da gabar ruwan kasar.
Wallafawa ranar:
Talla
Mai magana da yawun Haftar Khalifa Obeidi, ya ce umurnin ya fara aiki ne daga jiya, lamarin da kuma ake ganin cewa ya yi hannun riga da wani umurnin da firaministan kasar mai samun goyon bayan MDD Fayez al-Sarraj ya dauka ne, wanda ya bukaci kasashen duniya su aike da jami’an tsaron ruwansu domin hana baki tashi daga gabar ruwan zuwa Turai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu