'Yan Adawa Na Kasar Zimbabwe Na Shirin Hadewa Don Kawar Da Mugabe
Jagoran Babbar Jam'iyar adawa a kasar Zimbabwe Morgan Tsvangarai ya sanar da hada kai da tsoffin na kusa da Shugaba Roert Mugabe domin zame masa karfen kafa da kawo karshen mulkin na sa a babban zaben shekara mai zuwa.
Wallafawa ranar:
Tun shekara ta 1980 ne dai Shugaba Mugabe ke karagar mulki kuma duk da cewa ya haura shekaru 93 da haihuwa Jam'iyar ta sa ta sake tsayarda shi takaran shekara mai zuwa.
Yayin gangami da aka gudanar jiya Asabar Babbar Jam'iyar Adawa Movement for Democratic Change karkashin jagorancin Morgan Tsvangarai ta bayyanawa magoya bayan ta cewa ta shiga kawance da wasu tsoffin mataimakan shugaba Robert Mugabe da Jam'iyar ZANU-PF daga karagar mulki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu