Isa ga babban shafi
Saliyo

Saliyo ta shiga zaman makoki

Kasar Saliyo ta fara zaman makoki na mako guda sakamakon bala’in da ya afkawa kasar wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 300.

Shugaba Ernest Bai Koroma na Saliyo lokaci duba irin asarar da ambaliyar ruwa ta tafka a kasar
Shugaba Ernest Bai Koroma na Saliyo lokaci duba irin asarar da ambaliyar ruwa ta tafka a kasar SAIDU BAH / AFP
Talla

Shugaban kasar Ernest Bai Karoma ya ce za’a sauke tutocin kasar, yayin da ya bukaci taimakon kasashen duniya domin tallafawa wadanda hadarin ya ritsa da su.

Hukumomi sun ce ya zuwa yanzu yara 105 suka mutu, yayin da ake neman wasu mutane 600 da suka bata.

Kazalika wasu rahotanni na cewa gawawaki na rubewa.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce tana nazarin irin agajin da zata aikewa mutane kasar.

Kasar Israila da Hukumar Samar da Abinci ta WFP sun aike da kayan abincin da suka hada da shinkafa da man girki da za’a rabawa mutane 7,500 na makwanni biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.