Isa ga babban shafi
Africa ta Kudu-Zimbabwe

Afrika ta Kudu ta bai wa Grace Mugabe kariyar Diflomasiya

Gwamnatin Kasar Afirka ta kudu tace ta baiwa Uwargidan shugaban Zimbabwe Robert Mugabe kariyar diflomasiya, domin kaucewa tuhumar da ake mata na lakadawa wata mata duka a Johannesburg.

Grace Mugabe Uwargidan shugaban Zimbabwe, Robert Mugabe.
Grace Mugabe Uwargidan shugaban Zimbabwe, Robert Mugabe. REUTERS/Philimon Bulawayo
Talla

Ministar kula da harkokin waje na Africa ta Kudu, Maite Nkoana Mashabane, tace daukar matakin abin ne mai wuya amma babu yadda suka iya.

Tuni Grace Mugabe da maigidanta suka koma Zimbabwe bayan ya kammala halartar taron kasashen dake yankin kudancin Afirka.

Tun bayan lakadawa matar duka, tare da ji mata rauni Grace Mugabe ta fara wasan ‘yar buya da jami’an tsaro, inda ko a ranar Asabar din da ta gabata, taki halartar taron shugabannin a lokacin da aka fara shi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.