Isa ga babban shafi
Nijar

An bukaci mutane su kaucewa gidajensu a Yamai saboda ambaliya

Hukumomin Jamhuriyar Nijar sun bukaci dubban mazauna yankin birnin Yammai da ke fuskantar barazanar ambaliyar ruwa su kauracewa gidajensu sakamakon ruwan saman da ake ci gaba da tafkawa a birnin.

Ambaliya ta yi barna a Nijar a bana
Ambaliya ta yi barna a Nijar a bana BOUREIMA HAMA / AFP
Talla

Gwamnan Yamai Soumana Ali Zataoua ya shaidawa al’ummar Yankunan da ke fuskantar barazanar ta kafar talabijin da su gaggauta ficewa daga gidajensu.

A karshen mako Katanga ta rufta da weani magidanci da dansa bayan ruwan sama da aka sashe sa’o’I ana makawa a Yamai.

Mazauna kusa da rafin Gountou-Yena a Yamai sun fi fuskantar barazanar ambaliyar, yayin da gidaje sama da 300 suka rushe a Gabagoura.

Tun watan Yuni akalla mutane 41 suka mutu a sassan Nijar sakamakon ambaliyar ruwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.