Isa ga babban shafi
Mali

Mali: An kaddamar da cibiyar rundunar sojin kasashe 5

Shugaban kasar Mali Ibrahim Boubacar Keita, ya kaddamar da cibiyar rundunar sojin kasashe 5 da zasu yi yaki da kungiyoyin ‘yan ta’adda a yankin Sahel.

Wasu daga cikin dakarun kasar Mali.
Wasu daga cikin dakarun kasar Mali. Anthony Fouchard/RFI
Talla

An sanya cibiyar ne a Sevare dake tsakiyar kasar Mali, wadda ke da nisan kilomita 10 daga gabashin Mopti, a yankunan da ake fama da tashin hankali.

Rundunar mai bataliya 5, zata kunshi dakaru 5,000 da zasu fito daga kasashen Nijar, Chadi, Mali, Mauritania da kuma Burkina Faso.

Za kuma a rika warewa rundunar kasafin kudi na Dala miliyan 496 kowacce shekara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.