Tsohon Shugaban kasar Cote D'Ivoire na fatan sauyi a zaben 2018
A Cote D’ivoire jam’iyyar PDCI mai kawance da jam’iyyar Shugaban kasar RDR, ta bakin shugaban ta tsohon Shugaban kasar Henri Konan Bedie, na sa ran a samu sauyi ta fuskar shugabancin kasar Cote d’Ivoire.
Wallafawa ranar:
Bedie ya bayyana haka ne gaban duban magoya bayan jam’iyyar tareda cewa a lokacin zaben 2011, sun cimma matsaya ta cewa a shekara ta 2020,jam’iyya mai ci a yanzu za ta mika ragama zuwa jam’iyyar da ta mara masu a zaben da ya gabata, sabili da haka magoya bayan shugaban kasar su daina kawo rudani ga salon tafiyar siyasar gungun jam’iyyoyi da suka dafawa Shugaban kasar Ouattara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu