Isa ga babban shafi
Myanmar

MDD ta damu da tabarbarewar lamurra a Myanmar

Babban magatakarda na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, ya bayyana damuwarsa kan halin tabarbarewar lamurra a kasar Myanmar, inda ya bukaci kawo karshen matakan soji da gwamnati ke yi kan ‘yan kabilar Rohingya.

Magatakarda na MDD, António Guterres.
Magatakarda na MDD, António Guterres. REUTERS/Lucas Jackson
Talla

Yayin jawabinsa ga kwamitin Sulhu, Guterres ya bayyana cewa matsalar Myanmar ta haifar da ‘yan gudun hijira sama da rabin milyan, wadanda suka tsere zuwa Bangladesh, inda ya ke cewa ba za su amince da haka ba.

 

Shirin kai jami’an Majalisar Dinkin Duniya zuwa Jihar Rakhine da Myanmar don gane wa idanunsu abin da ke faruwa ya rushe, bayan da gwamnatin kasar ta sauya matsayin ta a kai.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.