Nadin manyan jami'ai a babban bankin Najeria CBN
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya aike wa majalisar dattawan kasar da wasikar neman izininta domin nada wasu manyan jami’ai a Babban Bankin kasar CBN.
Wallafawa ranar:
Daga cikin wadanda shugaban ke son nadawa sun hada da Aishah Ahmad a matsayin mataimakiyar gwamnan bankin.
Har ila yau akwai wasu mutane hudu da shugaban kasar ya nemi amincewar majalisar domin nada su a matsayin mambobin kwamitin tsara siyasar kudade a bankin na CBN.
Mutanen su ne Adeola Adenikinju, Aliyu Sanusi, Robert Asogwa da kuma Asheikh Maidugu, wadanda da zarar majalisar ta amince, mutanen za su fara aiki ne a cikin watan janairu mai zuwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu