Isa ga babban shafi
Afrika

An fara taro kan kokarin magance rikicin wasu kasashen Afrika

Rikicin kasashen Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo, Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, Burundi da kuma Sudan ta Kudu, su ne zasu mamaye taron kasashen Afirka 12 da za’ayi yau a birnin Brazzaville dake kasar Congo.

Taswirar wasu daga cikin kasashen tsakiyar nahiyar Afrika da ke fama da rikici.
Taswirar wasu daga cikin kasashen tsakiyar nahiyar Afrika da ke fama da rikici. Latifa Mouaoued/RFI
Talla

Taron wanda zai gudana a karkashin kungiyar da ake kira Great Lakes zata hada da shugabannin kasashen Angola, Kenya, Rwanda, Sudan, Tanzania, Uganda da kuma Zambia.

Jami’an tsaro da suka hada da na ‘yan sanda da manyan hafsoshin soji, sai kuma ministocin harkokin wajen kasashen, sun kwashe kawanaki biyu suna tattaunawa domin shirya jadawalin da shugabanin kasashen zasu duba.

A watan yunin shekara ta 2016 ne kasashen da ke kiran yankinsu da Great Lakes a turance suka gudanar da makamancin wannan taro.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.