Nijar ta tabbatar da ficewar Sojojin Chadi a Diffa
Hukumomin Jamhuriyar Nijar sun tabbatar da ficewar sojojin Chadi da ke yaki da kungiyar Boko Haram a Yankin Diffa, tare da cewa sun janye ne kada kadan a watanni shida.
Wallafawa ranar:
Barkai Issofou, ministan da ke kula da huldar jama’a ya tababtar da haka a gaban ‘Yan Majalisun kasar wadanda suka sake tsawaita dokar ta bacin da aka kafa a Yankin.
Ministan ya ce yanzu haka sojojin Nijar sun maye gurbin na Chadi domin samar da tsaro a Jihar ta Diffa.
Shugaban Nijar Mahamadou Issoufou ne ya nemi taimakon Chadi domin yakar Boko Haram bayan harin da ‘yan ta’addar suka kai a yankin Bosso inda mutane 26 suka mutu da suka hada da Sojojin kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu