Isa ga babban shafi
Kenya

Zaben Kenya: Kasashen yammaci na Fargaba

Jakadun kasashen Yammacin Duniya a birnin Nairobi na Kenya, sun bayyana furgbansu dangane da halin da kasar Kenya za ta iya fadawa sakamakon yadda lamurra suka zafafa kafin zaben shugabancin kasar na jibi alhamis.

Shugaban Kenya Uhuru Kenyatta
Shugaban Kenya Uhuru Kenyatta REUTERS/Thomas Mukoya
Talla

Jakadan Amurka Robert Godec wanda ke zantawa da manema labarai jim kadan bayan fitar da sanarwar hadin-gwiwa da jakadun suka fitar a jiya litinin, ya ce alhaki ya rataya a wuyan ‘yan siyasa domin su kwantar da hankulan magoya bayansu domin kaucewa rikici a lokacin zaben.

Shugaban 'yan adawa da ya janye takararsa Raila Odinga ya yi barazanar kaddamar da zanga-zanga a ranar zaben.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.