Kenya
Uhuru Kenyatta ya lashe zaben Kenya
Shugaban Hukumar Zaben Kenya, Wafula Chebukati ya bayyana shugaba Uhuru Kenyatta a matsayin wanda ya lashe zaben kasar da kuri’u sama da kashi 98 bayan janyewar ‘yan adawa.
Wallafawa ranar:
Talla
Bayanai sun ce kashi kusan 39 na masu kada kuri’u suka shiga zaben, kuma Kenyatta ya samu kuri’u miliyan 7 da 483,895.
Zaben Kenya ya jefa kasar cikin rikicin tsawon watanni biyu bayan kotun koli ta soke zaben da ya bai wa Kenyatta nasaran farko a ranar 8 ga Watan Agusta.
Chebukati da ya bayanan shaku kan sahihanci maimacin zaben ya tabbatar da ingancin sakamakon na wannan lokaci.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu