Sahel
Rundunar G5 Sahel ta soma aiki
Kasar Faransa ta ce rundunar kasashen Afirka da aka kafa a Yankin Sahel domin yaki da ‘yan ta’adda ta fara aiki wannan larabar.
Wallafawa ranar:
Talla
Wani sojin Faransa Kanar Marc-Antoine da ke aiki a Mali, ya ce tun safiyar wannan larabar aka fara girke sojojin kasashen Mali da Nijar da Burkina Faso domin gudanar da aikin.
Jami’in ya ce tuni aka girke daruruwan sojoji a matakin farko daga cikin sojoji 5,000 da ake saran za suyi aikin.
Kasar Faransa na da dakaru akalla 4,000 a Mali domin samar da tsaro.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu