Isa ga babban shafi
Sudan

Sabon rikici ya barke a Sudan ta Kudu

Barkewar wani sabon rikici a Sudan ta kudu ya dakushe kimar yarjejeniyar zaman lafiyar da aka kulla tsakanin bangarorin da ke rikici a kasar, abinda ya tilastawa dimbin Yan gudun hijira tserewa zuwa Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo domin samun mafaka.

Mai Magana da yawun Yan Tawayen SPLA, Lam Paul Gabriel ya yi zargin cewar sojoji dauke da tankunan yaki da kuma muggan makamai ne suka kai hari Lasu wanda ta ke cibiyar shugaban Yan Tawaye Riek Machar.
Mai Magana da yawun Yan Tawayen SPLA, Lam Paul Gabriel ya yi zargin cewar sojoji dauke da tankunan yaki da kuma muggan makamai ne suka kai hari Lasu wanda ta ke cibiyar shugaban Yan Tawaye Riek Machar. REUTERS
Talla

Yunkurin karbe iko da Lasu, daya daga cikin tungar Yan Tawaye na zuwa ne a dai dai lokacin da bangarorin da ke rikicin kasar ke sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a birnin Adis Ababa na Habasha wadda ake saran za ta fara aiki a karshen wannan mako.

Yan Tawayen sun sha alwashin sake kwace iko da garin wanda ya fada hannun sojojin gwammnati, matakin da ke jefa fargabar dorewar yarjejeniyar da aka sanyawa hannu.

Mai Magana da yawun Yan Tawayen SPLA, Lam Paul Gabriel yayi zargin cewar sojoji dauke da tankunan yaki da kuma muggan makamai ne suka kai hari Lasu wanda ta ke cibiyar shugaban Yan Tawaye Riek Machar.

Jami’in ya ce bangarorin biyu sun yi musayar wuta na dogon lokaci a tsakanin su.

Sai dai kakakin sojin kasar Santo Domic Chol ya yi watsi da zargin cewar su ne su ka kaddamar da harin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.