Isa ga babban shafi
Najeriya

Gwamnatin Najeriya za ta janyo hankulan al’ummar kasar zuwa aikin gona

Daya daga cikin muhimman matakan da gwamnatin Muhammadu Buhari ta dauka don janyo hankulan al’ummar kasar zuwa ga aikin gona shi ne hana shigo da kayyakin abinci daga ketare.Daukar matakin dake zuwa a dai-dai lokacin da ake fuskantar  rikici tsakanin manoma da makiyaya a wasu yankunan kasar.

Yankin da ake noman Shinkafa
Yankin da ake noman Shinkafa ISSOUF SANOGO / AFP
Talla

Wasu daga cikin yan kasar na ganin cewa kafin daukar irin wannan mataki, kamata ya yi ta inganta bangaren aikin gona da kuma samar wa manoma abubuwan da suke bukata.

Idan aka yi tuni a yan watanni da suka gabata gwamnatin Najeriya ta umurci jami’an Kwastam da su mayar da hankali zuwa kayakin abinci da ake shigo da su kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.