Bakin-haure 99 sun hallaka a tekun Libya
Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya, ta ce akalla bakin-haure 99 ne suka hallaka a tekun Llibya, sakamakon kifewar da jirginsu ya yi.
Wallafawa ranar:
Wasu bakin-haure uku da suka tsira, sun ce mafi akasarin wadanda suka nutse a tekun ‘yan kasar Pakistan ne, da akwai kuma wasu da suka fito daga kasar ta Libya.
An dai kwashe shekaru dubban bakin-haure suna bi ta kasar Libya a kokarinsu na ketarawa zuwa kudancin nahiyar Turai ta teku, sai dai kasashen nahiyar suna ci gaba da kokarin rage kwarar bakin-hauren.
A shekarar da ta gabata, kungiyar tarayyar turai EU, ta cimma wata yarjejeniya da ma’aikatan gabar ruwan Libya, wadda a karkashinta zasu taimaka, wajen datse yunkurin bakin hauren na kai wa turai, tare da mayar da su kasar ta Libya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu